in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hare-haren kunar bakin wake da aka kai a sansanin 'yan gudun hijira a Najeriya sun hallaka mutane a kalla 7
2017-07-24 19:29:31 cri

Rahotanni daga Najeriya na cewa, a kalla mutane bakwai ne suka gamu da ajalinsu kana wasu 15 kuma suka jikkata sakamakon wasu hare-haren kunar bakin wake da aka kaddamar jiya da dare a sansanonin 'yan gudun hijira dake kusa da garin Maiduguri a yankin arewa maso gabashin kasar.

Wani ganau da ya bukaci a sakaye sunansu ya bayyana cewa, wasu mata 'yan kunar bakin wake ne suka kaddamar da hare-haren a sansanin 'yan gudun hijira na Dalori mai nisan kilomita 4 daga Maiduguri, fadar mulkin jihar Borno, lokacin da galibin 'yan gudun hijirar ke barci.

Sai dai har yanzu jami'an tsaro a jihar Borno ba su tabbatar da aukuwar hare-haren ba. Amma mazauna yankin na cewa, da alamun kungiyar Boko Haram ce ta kai wadannan hare-hare. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China