in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hare-haren Boko Haram na sanya malaman jami'ar Maiduguri barin aiki
2017-08-07 19:32:47 cri
Rahotanni daga Najeriya na cewa, kimanin malamai 70 ne suka ajiye aikinsu a jami'ar Maiduguri dake yankin arewa maso gabashin kasar, sakamakon hare-haren baya-bayan da mayakan Boko Haram suka kai a kan jami'ar da ma'aikatanta .

Shugaban kungiyar malaman jami'o'i reshen jami'ar Maiduguri(ASUU)Dani Mamman ya bayyana cewa, galibin malaman da suka ajiye aikin nasu farfesoshi ne, da suka kware a fannonin bincike da koyarwa a jami'ar.

Mamman ya kuma shaidawa manema labarai a ranar Asabar din da ta gabata cewa, daya daga cikin dalilan da suka harzuka malaman barin jami'ar shi ne, harin baya-bayan da Boko Haram ta kaiwa abokan aikinsu, inda aka kashe malaman jami'ar biyar kana har yanzu ba a ji duriyar wasu uku da kungiyar ta yi garkuwa da su ba.

A makonni biyu da suka gabata ne dai mayakan Boko Haram suka yiwa malaman jami'ar kwanton bauna a yayin da suke aikin binciken mai tare da ma'aikatan hukumar samar da mai ta Najeriya a yankin tafkin Chadi.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China