in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sudan: An kaddamar da kwace makamai daga fararen hula a yankin Darfur
2017-08-08 09:41:03 cri
Gwamnatin Sudan ta kaddamar da wani shiri na karbe makamai daga hannun mayakan sa kai da fararen hula a yankin Darfur, da kuma raba al'ummar yankin da ababen hawa marasa lasisi, a wani mataki na aiwatar da matakan wanzar da tsaro.

Da yake tabbatar da hakan yayin wani taro da manyan hafsoshin tsaron kasar, da ma sauran mahukunta a birnin El Fasher, fadar mulkin jihar Arewacin Darfur, mataimakin shugaban kasar Sudan Hasabo Mohamed Abdul-Rahman, ya ce gwamnati na fatan ganin an raba daukacin fararen hular yankin da bindigogi marasa rajista, da sauran ababen hawa marasa lasisi. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China