in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sakamakon farko ya nuna cewa Paul Kagame ya samu nasarar lashe zaben shugaban kasar Rwanda a karo na 3
2017-08-05 17:29:15 cri
Hukumar zabe ta kasar Rwanda ta ce sakamakon farko na kuri'un da aka kidaya ya nuna cewa, shugaba mai ci Paul Kagame, ya lashe zaben shugaban kasar da aka jiya Juma'a da gagarumin rinjaye

Sakamakon da hukumar ta fitar ya nuna cewa, Paul Kagame ya lashe zaben da kaso 98.66 na kashi na kuri'un da aka kada.

Abokan adawarsa da suka hada da dan takara mai zaman kansa Phillippe Mpayimana da Frank Habineza na jam'iyyar Democratic Green sun samu kaso kasa da 1, inda hukumar zaben ta ce masu kada kuri'a miliyan 5.5 daga cikin miliyan 6.9 ne suka yi zaben.

Paul Kagame wanda ya nemi mulki a karo na uku, ya mika godiya ga magoya bayansa, a lokacin da yake jawabi a hedkwatar jam'iyyarsa ta RPF.

Ya ce a bayyane yake cewa jam'iyyar RPF ce ke da nasara, yana mai jinjinawa magoya bayansa da suka sake zabarsa dan sake mulkin kasar a karo na 3. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China