in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Manyan jaruman fina-finan Afrika za su hadu a Kigali cikin wannan watan
2017-06-10 12:22:01 cri
A karon farko, Rwanda za ta karbi bakuncin bikin bada lambar yabo ga jaruman fina-finan Afrika na bana.

Wata sanarwa da masu shirya bikin suka fitar a jiya Juma'a, ta ce za a gudanar da bikin na dare ne a ranar 24 ga watan nan a cibiyar baje koli ta Kigali, wanda ake kira da Kigali Camp, kuma wadanda za su karbi lambar yabon sun hada da fitattun masu shirya fina-finai da jarumai maza da mata a matakai 28.

Bikin na zaman wani gagarumin taro na masana'antar shirya fina-finai, kuma babban taron da zai samu halartar masu ruwa da tsaki kan harkar shirya fina-finan a nahiyar Afrika.

Cibiyar bada lambar yabo ta Afrika wato AMAA wadda aka kafa a shekarar 2005 da nufin ciyar da harkokin shirya fina-finai gaba a Afrika ce ta shirya bikin.

Wandanda aka zaba da a cikinsu za su samu lambar yabo su 155 ne ake sa ran za su hallara a Kigali domin bikin na bana.

Fitattun jaruman wasa 'yan Nijeriya kamar Ramsey Nouah da masu bada umarnin da shirya Fina-finai da suka hada da Lydia Forson 'yar kasar Ghana da Emem Isongo, Nkem Owoh, Rita Dominic na Nijeriya ne ake sa ran suma za su halarci bikin. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China