in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ghana ta lashi takobin yaki da masu safarar namun daji
2017-08-05 12:41:32 cri
Hukumomin a kasar Ghana sun yi gargadin cewa, za su dauki tsattsauran hukunci kan masu safarar namun daji dake ratsawa ta kasar.

Da yake ganawa da manema labarai a jiya Jumma'a, diraktan zartaswa na sashen kula da namun dawa na hukumar lura da gandun daji ta kasar Nana Kofia Adu-Nsiah, ya shaidawa manema labarai cewa, hukumomi ba za su lamuncewa duk wani dake kokarin amfani da kasar a matsayin wajen yada zagon yayin da yake safarar namun daji ba.

Nana Kofia Adu Nsiah, ya bayyana haka ne lokacin da yake mai da martani ga labaran da ake yadawa a kafofin watsa labarai na kasashen ketare game da kwace kilogram 393.50 na kwanson dabbar pangolin a kasar Malaysia cikin watan Yunin bana, wanda ake zargin ya fito daga Ghana.

Ya kara da cewa, a bayyane yake masu safarar namun daji na amfani da Ghana a matsayin wajen yada zango yayin da suke gudanar da mummunan aikinsu.

A don haka, suke son aikewa da sako da kakkausar murya gare su cewa, ba su da muhalli a Ghana, yana mai cewa za su zakulo su.

Har ila yau, ya jadadda cewa za a kara karfafa hadin gwiwa tsakanin jami'an hana fasa kauri da na 'yan sanda da jami'an filayen jirgin sama da jami'an sirri kaya domin kawo karshen al'amarin. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China