in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ghana ta kafa dakarun tsaro na hadin gwiwa don maganace hakar ma'adinai ba bisa ka'ida ba
2017-08-01 10:59:20 cri
Gwamnatin kasar Ghana ta kafa wata rundunar tsaro ta hadin gwiwa tsakanin sojoji da 'yan sanda, domin magance hakar ma'adinai ba bisa ka'ida ba.

An tura runduna mai mambobi 400 da aka kafa a jiya zuwa yankunan Ashanti da gabashi da yammacin kasar, inda ayyukan suka fi kamari.

Shugaban kasar Ghana Nana Akufo-Addo ya jadadda kudurin gwamnatinsa na kawo karshen hakar ma'adinai ba bisa ka'ida ba.

Kaddamar da rundunar mai suna "Operation Vanguard" ya zo ne kasa da wata guda bayan mutane 24 sun fada tare da mutuwa a cikin wani ramin hakar ma'adinai a yankunan Ashanti da yammacin kasar.

Bayan bikin kaddammar da rundunar, Ministan muhalli da kimiyya da fasaha da kirkire-kirkire na kasar Kwabena Frimpong Boateng, ya bukaci dakarun sun gudanar da ayyukansu bisa biyayya ga doka tare da kauracewa take hakkokin mazauna yankunan.

Ana sa ran rundunar za ta kasance a yankunan har zuwa lokacin da za a farfado da yankunan da koguna da suka lalace da kuma cimma shirin farfado da dazuka. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China