in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin Ghana ta kaddamar da shirin bunkasa sana'o'i na dala miliyan 10
2017-07-14 10:01:50 cri
Shugaban kasar Ghana Nana Akufo-Addo, ya kaddamar da shirin bunkasa masana'antu da cigaban fasaha na kudi kimanin dalar Amurka miliyan 10.

Shirin dai wani tsari ne da gwamnatin ta bullo da shi a matsayin wani muhimmin tsari da zai taimakawa wadan da za su kakkafa kananan masana'antu da kasuwanci a kasar.

Baki daya manufar wannan shiri shi ne domin bunkasa bangaren kamfanoni masu zaman kansu a matakin farko don ciyar da harkokin kasuwanci gaba da samar da guraben ayyukan yi ga matasan kasar Ghana, domin su samu hanyoyin da za su bunkasa kasuwancinsu.

Akufo-Addo ya ce, shirin zai kara baiwa sabbin nau'ikan kasuwanci damar bunkasuwa kuma zai samar musu hanyoyin samun jari da yadda kasuwancinsu zai bunkasa, da ba su kariya a lokacin da ake fama da rikicewar sha'anin cinikayya a shekaru da dama a kasar.

Shugaban na Ghana ya ce, shirin zai taimaka wajen kara hadewa bangarorin kasuwancin waje guda domin samun bunkasuwa da samar da ayyukan yi masu yawa a matakai na tarayyar kasar.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China