in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin kasar Ghana ta zurfafa matakan cike gibi da karuwar basussuka yayin bitar kasafin kudin kasar na tsakiyar shekara
2017-08-01 10:02:24 cri
Gwamnatin kasar Ghana ta kara daukar matakai kan wasu muhimman sassan tattalin arzikin kasar da take fatan cimma wasu alkaluma a kasafin kudin wannan shekara, a wani mataki na cike gibin da tattalin arzikin kasashe yake fuskanta.

A jawabinsa na farko yayin bitar kasafin kudin kasar na rabin shekara a gaban majalisar dokokin kasar, ministan kudin kasar Ken Ofori-Attah, ya bayyana cewa, an sake rage kudaden da za a kashe ta yadda zai yi kasa da yawan kudaden haraji da aka yi hasashen tarawa, ta yadda zai yi daidai da abin da aka kasafta a tsarin kasafin kudin kasar.

Ministan ya ce an kuma sake rage kudaden haraji da tallafi da aka yi hasashen samu ya zuwa kaso 0.9 cikin 100 na alkaluman GDPn kasar, wato daga kudin kasar Cedi biliyan 44.5 kwatankwacin dala biliyan 10.11 zuwa Cedi biliyan 43.1. Bugu da kari, an rage jimmalar kudaden da aka yi hasashe kashewa da kaso 1.1 cikin 100 na GDPn kasar wato daga Cedi biliyan 58.1 zuwa Cedi biliyan 55.9.

Ya ce, bayan gudanar da wadannan gyare-gyare, ana fatan gibin kasafin kudin kasar zai ragu daga Cedi biliyan 13.2 wato kaso 6.5 cikin 100 na alkaluman GDPn kasar, zuwa Cedi biliyan 12.8 cikin 100, kaso 6.3 cikin 100 ke nan na alkaluman GDPn kasar ta Ghana.

Ko da yake ba a canja hasashen da aka yi game da samun karuwar kaso 6.3 cikin na GDP a wannan shekara ta 2017 ba, amma ministan ya sanar da rage hasashen ci gaban GDPn daga Cedi biliyan 203.41 zuwa Cedi biliyan 202.01. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China