in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Trump ya rattaba hannu kan dokar sanya takunkumi kan kasashen Rasha, Iran da Koriya ta arewa amma ya soki dokar
2017-08-03 10:46:51 cri
Shugaban Amurka Donald Trump ya rattaba hannu kan dokar kakabawa kasashen Rasha, Iran da Koriya ta arewa (DPRK) takunkumi, sai dai ya soki lamirin dokar inda ya bayyana cewa akwai manyan kura kurai a cikinta.

A wata sanarwar da fadar White House ta fitar, Trump ya bayyana cewa duk da cewa matakai ne da aka dauka domin ladaftarwa kan kasashen Iran da DPRK kuma matakin yana son bayyanawa Rasha karara cewa, Amurka ba za ta taba lamuntar duk wani yunkuri na yin shishshigi cikin harkokinta na siyasa ba, sai dai ya kalubalanci dokar da cewa ta kunshi wasu batutuwa da suka saba tanade-tanaden kundin tsarin mulkin kasar, kuma a cewarsa wannan babban kuskure ne.

A farkon wannan wata ne dai kudurin dokar ya samu amincewar majalisar dokokin kasar ta Amurka, duk kuwa da bukatar da gwamnatin Trump ta nuna na neman majalisar ta yi sauye sauye kan dokar sakamakon alakar dake tsakanin Amurkar da Rasha. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China