in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasashen BRICS sun hada kai wajen yaki da shingayen cinikayya masu tsauri
2017-08-03 10:11:47 cri
Ministocin ciniki na kasashen BRICS wato kungiyar kasashe masu samun ci gaban tattalin arziki cikin sauri, sun amince da yin adawa da shingayen cinikayya masu tsauri tare da kare tsarin cinikayya tsakanin kasashe.

Ministocin sun dauki wannan mataki ne jiya, bayan kammala taronsu na shekara da ya gudana a Shanghai na kasar Sin.

Wata sanarwa da suka fitar bayan taron ta ce, dukkan kasashen kungiyar da suka hada da Brazil da Rasha da Indiya da Sin da Afrika ta kudu mambobi ne na Hukumar WTO mai kula da harkokin cinikayya ta duniya, wadanda kuma ke taka muhimmiyar rawa wajen bunkasa tattalin arzikin duniya.

Ministocin sun kuma yi kira da sauran kasashe su bi sahunsu wajen yaki da shingayen cinikayya, suna masu karfafa musu gwiwar shiga a dama da su cikin hukumar WTO, inda kuma suka bukaci hukumar ta kara mai da hankali kan kasashe masu tasowa.

Kasar Sin dake rike da shugabancin kungiyar BRICS a bana, za ta karbi bakuncin babban taron kungiyar karo na 9 cikin watan Satumba mai zuwa a Xiamen na lardin Fujian. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China