in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kira taron manyan jami'an tsaron kasashen kungiyar BRICS a Beijing
2017-07-28 18:09:30 cri

A yau Jumma'a 28 ga wata ne, aka bude taron manyan jami'an tsaron kasashen kungiyar BRICS karo na 7 a nan birnin Beijing, wanda ya kasance daya daga cikin jerin tarukan da kasar Sin ta kira yayin da take shugabancin kungiyar BRICS a bana, haka kuma taron wani muhimmin dandali ne ga kasashen kungiyar inda suke tattauna batutuwan da suka shafi hadin gwiwa ta fuskar tsaro.

A yayin taron, bangarori daban daban sun amince da cewa, za a kara kyautata tsarin taron don inganta hadin gwiwar kasashen a fannonin siyasa da tsaro. Kuma za a yi kokarin kyautata aikin daidaita lamuran duniya, da tinkarar barazara da kalubalolin da duniya ke fuskanta, ta yadda za a ciyar da dokokin kasa da kasa zuwa gaba. Bugu da kari,kasashen kungiyar za su inganta hadin kansu wajen yaki da ta'addanci, tsaron Intanet, da ma tsaron makamashi.(Kande Gao)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China