A yau ne dan majalisar zartarwar kasar Sin Mr. Yang Jiechi ya gana bi da bi da manyan jami'an tsaro daga kasashen Afirka ta kudu, Brzail da kuma India wadanda ke halartar taron manyan wakilan kasashen BRICS kan harkokin tsaro karo na 7 dake gudana a nan birnin Beijing, fadar mulkin kasar Sin
A yayin ganawar Mr. Yang ya bukaci kasashen kungiyar ta BIRCS da su zurfafa hadin gwiwa a fannonin sadarwa, da mutunta juna, da siyasa da batutuwan da suka shafi tsaro, da martaba dokokin kasa da kasa da yayata hadin gwiwa a fannoni daban-daban domin amfanin al'ummomin dukkan kasashe mambobin kungiyar, kana su kasance masu martaba muradun juna. (Ibrahim)