in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Uganda tana zaman makokin dakarun wanzar da zaman lafiya da aka kashe a Somalia
2017-08-03 09:58:30 cri
Jirgin sama dauke da gawawwakin dakarun kiyaye zaman lafiya wadanda aka kashe a Somalia sun isa filin jirgin sama na Entebbe na kasar Uganda a ranar Laraba, a yayin da iyalai da dangin mamatan ke ci gaba da nuna alhininsu.

Kimanin dakarun wanzar da zaman lafiya 'yan kasar Ugandan 12 ne mayakan Al-Shabaab suka hallaka a Somaliya, kana wasu dakarun 9 kuma aka raunata.

Birgediya Richard Karemire, mai magana da yawun rundunar sojin kasar Uganda ya shedawa 'yan jaridu cewa, mutuwar abokan aikin nasu ba zai sanyaya musu gwiwa ba wajen murkushe mayakan kungiyar ta Al-Shabaab.

A ranar Talata ne rundunar sojin kasar Ugandan ta kafa hukumar binciken musabbabin mutuwar dakarun.

Kasar Uganda ta bada gudumowar sojoji kimanin 6,500 daga cikin adadin sojojin kiyaye zaman lafiya 22,000 na tarayyar Afrika dake aiki a Somalia. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China