in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Uganda ya bukaci kasashen duniya su hada kai da nufin tabbatar da zaman lafiya
2017-02-19 12:15:10 cri
Shugaban kaar Uganda Yoweri Museveni, ya bukaci shugabannin kasashen yamma, su mai da hankali wajen tabbatar da hadin kan kasa da kasa maimakon siyasar rarrabuwar kawuna dake barazana ga zaman lafiya a duniya.

Cikin wata sanarwa da aka raba ga kafafen yada labarai, Shuagaba Museveni ya ce kasashen yamma masu ra'ayin sassauci na ci gaba da tafka kurakurai ta hanyar neman kakabawa al'ummar duniya ra'ayinsu.

Ya ce wadannan ra'ayoyi sun shafi zaman takewar iyali da tsarin demokradiyya da luwadi da tattalin arziki da sauransu, al'amarin da ya ce na kawo rarrabuwar kawuna da rikici wajen magance al'amuran da suka shafi kasa da kasa.

Ya ce akwai batutuwa da ya kamata duniya ta mai da hankali kansu kamar ilimin zamani a fannin kimiyya da zamantakewa da karfafawa mata da cinikayya da yaki da masu tsatsauran ra'ayi da sauransu.

Ya ce ci gaba da sukar kasashen Rasha da Sin da masu sassaucin ra'ayin ke yi, ba zai haifar da da mai ido ba, yana mai cewa kasashen 2 sun himmantu wajen ragewa miliyoyin al'ummar Afrika radadin talauci.

Ya ce har ila yau, kasashen na taimakawa kasashen Afrika yaki da mulkin mallaka da mummanan tasirinsa. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China