in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An bude taron manyan jami'an AL da AU a kasar Masar
2017-08-03 09:27:53 cri
A jiya Laraba ne, aka bude wani taron manyan jami'ai da kungiyoyin masana na kungiyar kasashen Larabawa (AL) da takwaranta ta kungiyar tarayyar Afirka (AU) a birnin Alkahiran kasar Masar .

Da yake jawabi ga mahalarta taron, mataimakin babban sakataren kungiyar kasashen Larabawa mai kula da harkokin siyasar kasa da kasa Khalid al-Habas, ya ce manufar shirya wannan taro ita ce karfafa hadin gwiwa da tuntubar juna tsakanin sassan biyu, ganin yadda sassan ke da tsarin al'adu da bayanan tarihi iri daya.

A nata jawabin kwamishinar kungiyar tarayyar Afirka mai kula da harkokin jin dadin jama'a Amira al-Fadil, ta jaddada muhimmancin halartar tawagar kungiyar mai kunshe da kwararru a fannonin daban daban, wadanda ake fatan za su tattauna a wannan taro.

Ana fatan taron zai ba da shawarwari game da taron hadin gwiwar shugabannin kungiyoyin biyu da aka shirya gudanarwa a karshen wannan shekara ta 2017. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China