Da yake zantawa da manema labarai a Mogadishu, mai magana da yawun AMISOM Joe Kibet, ya tabbatar da cewa an kaddamar da harin amma ya musanta hallaka ko da soja guda a gundumar Bulaamareer dake yankin Lower Shabelle.
Ya ce sabanin rahotannin da kafafen yada labarai suka watsa inda suka danganta abin da mai magana da yawun Al-Shabaab Abdiasis Abu Musab wanda ya ce an kashe sojoji 39, ya ce adadin sojojin kasar dake cikin tagawar ba su ma kai yawan abin da aka yi ikirarin kashewa ba.
Kibet ya bayyana cewa yawancin bataliya guda ba ta wuce adadin sojoji 39.
Rahotannin da kafafen yada labarai suka watsa da wasu shafukan intanet suka wallafa ya nuna cewa Al-Shabaab ta yi ikirarin hallaka sojojin AMISOM 39 daga Uganda inda ta hallaka su saboda girman makamansu. (Ahmad Fagam)