in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane 16 sun rasu sakamakon fashewar boma-bomai a Afghanistan
2017-03-02 10:14:09 cri
Jiya Laraba, an ji fashewar boma-bomai har sau biyu a jere a Kabul babban birnin kasar Afghanistan.

Bayan aukuwar hare-haren, hukumar lafiya ta kasar ta tabbatar da cewa, hare-haren sun haddasa mutuwar mutane 16, tare da jikkata wasu 59, ciki har da yara da mata.

Bayan aukuwar lamarin, kungiyar Taliban ta sanar da daukar alhakin hare-haren.

Cikin kakkausar murya, shugaban kasar Ashraf Ghani ya yi allah wadai da wadananan hare-hare.

A 'yan kwanakin nan, damuwa ta yi tsanani game da yanayin tsaro a kasar Afghanistan, duk da cewa, dakarun kasar sun karfafa yaki da suke kai da 'yan adawa, har yanzu masu adawar da na ci gaba da kai hare-hare. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China