in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AU ta nemi a yi sauye-sauye don shawo kan kalubalolin kungiyar
2017-07-02 13:40:23 cri

Mataimakin kwamishinan gudanarwar kungiyar tarayyar Afrika AU Thomas Kwesi Quartey, ya bayyana cewa, samar da hadin kai wajen aiwatar da muhimman shirye-shiryen kungiyar ta AU mataki ne da zai haifar da gagarumin cigaba.

Quartey, ya shedawa 'yan jaridu a wajen taron kolin AU karo 29 a Addis Ababa na kasar Habasha cewa, idan aka samu nasarar aiwatar da sauye sauyen, zai taimakawa kasashen Afrika wajen shawo kan kalubalolin dake neman zama tarnaki wajen aiwatar da manufofin AU na cigaba.

A cewarsa hanyoyin samun kudade wani muhimmin bangare ne dake bukatar a yi masa kwaskwarima, domin baiwa kungiyar ta AU 'yancin cin gashin kanta ta fuskar gudanar da sha'anin kudi.

Dama dai shugabannin kasashen mambobin kungiyar ta AU sun rattaba hannu kan batun sauya fasalin kudi na kungiyar a lokacin taron kolin kungiyar karo na 27 da aka gudanar a kasar Ruwanda a bara.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China