in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Masu bore sun aukawa hedkwatar gyaran kundin tsarin mulkin kasar Libya
2017-07-31 10:21:58 cri
A ranar Asabar din da ta gabata ce masu zanga-zanga suka aukawa hedkwatar dake kula da aikin gyara kundin tsarin mulkin kasar Libya, bayan da hukumar da babban rinjaye ta amince a gabatar da daftarin kundin tsarin mulkin kasar.

Kakakin hukumar Sidiq Dersi ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Xinhua cewa, mambobin hukumar 43 ne suka gana a wannan rana domin kada kuri'ar tsara kundin tsarin mulkin kasar, biyo bayan gyaran da mambobin hukumar suka yiwa wannan kundi.

Dersi ya ce bayan ganawar ce sai daruruwan masu bore suka yiwa hedkwatar hukumar zobe, don nuna rashin amincewarsu da wannan mataki. Sai dai an dauki dukkan matakan da suka dace don kare lafiyar mambobin hukumar da ke wannan ganawa.

Shugaban majalisar dokoki mai mazauni a gabashin kasar Libya Agila Saleh, ya yi kira ga zaman majalisar da ya auna irin rawar da hukumar dake rubuta kundin tsarin mulkin kasar take takawa. Yana mai jaddada bukatar a kafa kwamitin kwararru yayin da ake kokarin yiwa kundin tsarin mulkin kasar gyaran fuska, saboda gazawar hukumar na gabatar da daftarin kundin tsarin mulkin kasar. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China