in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An saki Saif Al-Islam Gaddafi amma ba a san inda yake ba a halin yanzu
2017-06-11 13:49:36 cri
Masu tayar da kayar baya sun saki Saif Al-Islam Gaddafi, dan marigayi tsohon shugaban Libya Muammar Gaddafi, wanda suke tsare da shi a Zintan dake yammacin kasar.

Masu tayar da kayar baya dake yin biyayya ga huhumomin gabashi sun sanar a ranar Asabar cewa sun saki Saif Gaddafi ne a ranar Juma'a, kuma ya bar yankin Zintan tun tuni. Amma ba'a san takamamman inda yake ba a halin yanzu.

Sai dai kawo yanzu, gwamnatin Libyan ba ta ce uffan ba game da batun sakin nasa.

Ana tsare da Saif Gaddafi ne tun a shekarar 2011 a Zintan, garin ne dake yankin kudu maso yammacin babban birnin kasar Tripoli. Ana zarginsa ne da haddasa tashin hankali da kuma hallaka masu zanga zanga a lokacin tarzomar da ta barke a kasar a shekarar 2011 wadda ta yi sanadiyyar tunbuke mahaifinsa daga karagar mulkin kasar.

Wata kotu a Tripoli ta zartar da hukuncin kisa kan Saif Gaddafi, wanda a baya ake gani a matsayin wanda zai gaji mahaifinsa, an yanke masa hukuncin kisan ne tare da wasu tsaffin jami'an tsohuwar gwamnatin Libyan a shekarar 2015.

Sai dai kuma, majalsiar dake zamanta a gabashi, ta yi wa Saif Al-Islam din afuwa jim kadan bayan yanke masa hukuncin.

Kotun hukunta manyan laifukan yaki ta kasa da kasa ICC ita ma take neman Saif Gaddafi ruwa a jallo, bisa zarginsa da aikata cin zarafin bil adama a lokacin tarzomar kasar a 2011. Sai dai kuma mayakan sun ki amincewa su mika shi ga kotun ta ICC.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China