Firaministan kasar Libya da MDD ke marawa baya Fayez Serraj ya yi kiran da a gudanar da sabbin zabukan majalisar dokoki da na shugaban kasa a watan Maris din shekarar 2018. Zaben da firaministan ya ce zai baiwa 'yan kasar damar zabar sabon shugaban kasa da 'yan majalisun dokoki, kuma zaben ba zai shafi yarjejeniyar siyasar kasar da MDD ke marawa baya ba.
An dai nada gwamnatin hadin kan kasar Libya da Serraj ke jagoranta ne bisa yarjejeniyar shimfida zaman lafiya da MDD ta gabatar da nufin kawo karshen rarrabuwar kawunan siyasar kasar.(Ibrahim)