in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugabannin Libya sun amince su kawo karshen gaba da suke tare da gina tsarin demokradiyya
2017-07-26 13:45:12 cri
Shugabannin Libya masu adawa da juna, Fayez Al Sarraj shugaban Gwamnatin kasar dake da goyon bayan MDD da mai adawa da shi Khalifa Haftar jagoran kungiyar Libiyan National Army, sun amince su dakatar da bude wuta tare da gaggauta shirye-shiryen gudanar da zaben shugaban kasa nan ba da dadewa ba.

Cikin wata sanarwar hadin gwiwa, bayan kammla ganawa kan yunkurin kawo karshen tashin hankali a Libya, Fayez Al Sarraj da Khalifa Haftar, sun ce sun amince su daina bude wuta tare da kauracewa amfani da dakaru kan duk wani abu sabanin yaki da ta'ddanci, bisa biyayya da yarjejenioyin siyasa na Libya da na kasashen waje.

Bayan matsalar siyasa da yakin basasa da suka shafe lokaci mai tsawo, shugabannin biyu sun lashi takobin kawo karshen rikicin Libya, wanda suka ce na bukatar wani tsarin sulhu na kasa da zai kunshi dukkan al'ummar kasar ciki har da cibiyoyin da rundunonin tsaro wadanda suka shirya a dama da su. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China