in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rundunar sojin Libya na zargin kasashen Qatar da Sudan da Turkiyya da mara baya ga ayyukan ta'addanci a kasar
2017-07-05 09:40:06 cri
Kakakin rundunar sojin Libya Ahmed al-Mesmary, ya zargi kasashen Qatar da Sudan da kuma Turkiyya, da goyon bayan ayyukan ta'addanci a kasar da rikici ya daidaita.

Yayin wani taron manema labarai da ya gudana jiya a Cairo babban birnin kasar Masar, Ahmed al-Mesmary, ya ce goyon bayan ayyukan ta'addanci na nufin Qatar na aikata laifuffukan da suka take hakkin dan Adam a Libya.

Kakakin ya ce rundunar sojin ta samu nasara, sannan ita ke rike da ikon yankuna da yawa na Libya, duk da yaki da take da kungiyoyi 4 da suka hada da IS da Al-Qaeda da ta 'Yan Uwa Musulmi da kuma wasu kungiyoyin tsageru masu dauke da makamai. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China