in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
A kaddamar da bincike a kan yadda aka sako dan Gaddafi
2017-06-12 13:46:01 cri
Mukaddashin babban lauyan kasar Libya Ibrahim Masoud Ali ya bayyana a jiya Lahadi cewa, an fara gudanar da bincike a kan wadanda suke da hannun a sako Saif al-Islam Gaddafi, dan tsohon shugaban kasar ta Libya. marigayi Muammar Gaddafi.

Ali ya kara da cewa, za a gudanar da bincike tare da hukunta wadanda aka gano suna da hannu wajen kawo cikas ga yadda ake aiwatar da shari'ar da aka yanke wa Saif al-Islam Gaddafi.

Wata kungiyar 'yan tawaye ne ta ke tsare da Gaddafi, mai shekaru 45 a duniya tun shekarar 2011 a garin Zintan, da ke kudu maso yammacin birnin Tripoli. Ana zarginsa ne da tada tashin hankali da hallaka masu zanga-zanga a tarzomar da ta tashi a shekarar 2011, wadda ta yi sanadiyyar tunbuke mahaifinsa daga karagar mulki.

Wata kotu a Tripoli ta zartar da hukuncin kisa kan Saif Gaddafi, wanda a baya ake gani a matsayin wanda zai gaji mahaifinsa, an yanke masa hukuncin kisan ne tare da wasu tsoffin jami'an tsohuwar gwamnatin Libyan a shekarar 2015. Sai dai kuma, majalisar dokokin dake zamanta a gabashin kasar, ta yi wa Saif Al-Islam din afuwa jim kadan bayan yanke masa hukuncin. (Lubabatu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China