Jiya Asabar 29 ga wata, shehun malami Justin Yifu Lin na jami'ar Peking ta kasar Sin, wanda shi ne tsohon babban kwararren masanin tattalin arizki na Bankin Duniya ya bayyana a birnin Dar es Salaam, hedkwatar kasar Tanzaniya cewa, kasashen Afirka za su iya gaggauta yin kwaskwarima kan tsarin tattalin arzikinsu ta hanyar yin hadin gwiwa da kasar Sin, ta yadda za su samu saurin bunkasuwa.
Mista Lin ya fadi haka ne yayin da yake zantawa da manema labaru bayan da ya yi jawabi a babban bankin Tanzaniya a wannan rana. (Tasallah Yuan)