in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilin Sin ya yi kira a kara marawa kasahen tsakiya da yammacin Afirka baya
2017-01-13 13:13:53 cri
A jiya Alhamis ne, zaunannen mataimakin wakilin gwamnatin kasar Sin dake Majalisar Dinkin Duniya Wu Haitao ya yi kira ga kasashen duniya da su kara kokarin da suke yi na nuna goyon-baya ga kasashen dake yankin tsakiya gami da yammacin Afirka, ciki har da kasashen dake kewaye da tafkin Chadi, domin kawar da barazanar ta'addanci a wurin.

A jawabin da ya gabatar yayin taron kwamitin sulhun MDD kan halin da ake ciki a yankunan dake kewaye da tafkin Chadi, Wu ya bayyana cewar, aikin yaki da ta'addanci a Afirka, yana da muhimmanci ga ayyukan murkushe ta'addanci da ake yi a fadin duniya. Duk da haka, kamata ya yi kasashe daban-daban su taimakawa kasashen Afirka domin inganta karfin yaki da ta'addanci, bisa tushen mutunta 'yanci da mallakar cikakkun yankunansu, da kuma gudanar da ayyukan soji na hadin-gwiwar kasashe daban-daban, a wani kokari na kawar da barazanar 'yan ta'adda a yankin.

Mista Wu ya kuma jaddada cewar, kasar Sin na son hada kai tare da sauran kasashe, domin tallafawa kasashen dake tsakiya da kuma yammacin Afirka wajen samun ci gaba da zaman lafiya mai dorewa, da bayar da gudummawa ga bunkasar nahiyar Afirka baki daya.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China