in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jami'in kasar Sin: Cika alkawari ya fi muhimmanci wajen hadin gwiwa da kasashen Afirka
2016-08-29 15:21:04 cri
Zhang Ming, mataimakin ministan harkokin wajen kasar Sin, wanda ke halartar taron shugabannin kasashen Afirka da kasar Japan a birnin Nairobin kasar Kenya, a matsayin wani mai sa ido, ya shedawa manema labaru a jiya Lahadi cewa, yayin da ake gudanar da taruka kan hadin gwiwa da kasashen Afirka, bai kamata a yi alkawari da gabatar da buri kawai ba. Maimakon haka, ya kamata a yi kokarin cika alkawarin da aka dauka domin samar da ainihin moriya ga jama'ar kasashen Afirka.

A cewar jami'in na kasar Sin, ya kamata a mai da hankali kan sakamakon da aka cimma, da kuma matakan da aka dauka a maimakon alkawarin da aka yi, yayin da ake tantance huldar hadin gwiwa tsakanin wasu kasashe da kasashen Afirka. Sai dai a nata bangare, kasar Sin bisa matsayinta na wata kasa mai muhimmanci wanda ke jagorantar aikin hadin kai tare da kasashen Afirka, tana fatan ganin karin bangarori masu huldar hadin gwiwa tare da nahiyar Afirka. Ban da haka kuma, kasar Sin na son yin kokari tare da sauran bangarorin duniya wajen raya tattalin arziki da zamantakewar al'ummar Afirka, don neman samun ci gaba tare, gami da samun moriya ta bai daya.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China