in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Xi ya bukaci yin musayar sojoji tsakanin kasa da kasa don karfafa zaman lafiyar duniya
2017-07-30 09:48:24 cri
Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya ce yana fata dakarun sojin kasar Sin za su zurfafa yin musaya da takwarorinsu na sauran kasashen duniya domin karfafa hadin gwiwa da kuma ba da gudunmawa wajen tabbatar da zaman lafiya a duniya.

Cikin wani sakon faifan bidiyo da Shugaba Xi ya aikewa rundunar soji ta kasa da kasa wanda kasar Rasha ta kafa inda ta gudanar da gasanninta na shekarar 2017, Xi ya ce hadin gwiwar sojojin kasa da kasa zai kara tabbatar da amincewa tsakanin dakarun, kana zai tabbatar da zaman lafiya a matakan shiyya-shiyya da ma duniya baki daya.

Xi, wanda kuma shi ne shugaban hukumar tsakiya mai kula da sojoji wato CMC, ya aike da sakonsa na fatan alheri a madadin gwamnatin kasar Sin cikin faifan bidiyo.

An shirya gasar sojojin ne ta shekarar 2017, wanda za'a gudanar a ranar 12 ga watan Augusta, bikin ya kunshi wasanni 28 wanda ya hada da kasashen Rasha, Sin, Azerbaijan, Belarus da Kazakhstan. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China