Rahotannin da aka fitar a jiya, sun bayyana cewa, a daren ranar 27 ga wata, wasu bata gari sun kai hari ba zato ba tsammani kan wani kauye dake jihar Soum, wanda ya haddasa mutuwar wani dan majalisar dokokin birnin da iyalansa guda biyu, sannan suka kwace dabbobin da dama da mazauna kauyen ke kiwo.
Zuwa yanzu, Gwamnatin kasar Burkina Faso ba ta fitar da wata sanarwa game da harin ba, haka zalika babu wata kungiya da ta sanar da daukar alhakinsa.
Tun daga daren ranar 24 zuwa safiyar ranar 25 ga wata, wasu tsageru sun kai hare-hare kan kauyuka 3 na jihar Soum, wadanda suka haddasa mutuwar mutane a kalla 5.
Hukumar kiyaye tsaro ta kasar ta bayar da labarin cewa, mutanen 5 membobi ne na wata kungiyar masu tsattsauran ra'ayi. Kuma an yi zaton cewa, kungiyar ce ta kai hare-haren domin hukunta su. (Zainab)