in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Burkina Faso ta yi kira da a karfafa hadin kai tsakanin kasashen nahiyar Afirka domin inganata samun ci gaba
2017-03-17 10:08:37 cri
Shugaban kasar Burkina Faso, Roch Marc Christian Kabore, ya bukaci a gaggauta tare da karfafa hadin gwiwa tsakanin kasashen Afrika domin inganta ci gaban nahiyar.

Da yake jawabi jiya, yayin bude taron kasa da kasa kan bunkasa nahiyar Afrika a birnin Casablanca na kasar Morocco, Christian Kabore ya yi kira da kasashen Afika su hada hannu wajen tunkarar kalubalen da nahiyar ke fuskanta a dukkan bangarori, yana mai jadadda cewa, kamata ya yi manufofin tattalin arzikin yankin su mai da hankali ga masu karamin karfi da gajiyayyu.

Ya ce dole ne shugabnnin nahiyar da 'yan kasuwa da sauran masu ruwa da tsaki su dauki managartan matakai da za su taimaka wajen tabbatar da habakar tattalin arziki da kuma inganta walwalar al'umma ta yadda za a samu dawwamammen zaman lafiya a Afrika da ma duniya baki daya.

Taron na yini biyu mai taken 'sabbin manufofin ci gaba da ya kunshi dukkan bangarori a Afrika' ya samu mahalarta 1,500 daga kasashen nahiyar 25 da kuma wasu kasashe. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China