in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Burkina Faso za ta kare tsarin yada labarai a lokacin da take fuskantar barazanar tsaro
2017-04-23 12:48:53 cri
Hukumar yada labarai ta kasar Burkina Faso, ta kaddamar da wani shiri da zai kula da harkokin watsa labarai a lokacin da ake tsaka da fuskantar rikicin ta'addanci a kasar.

Cikin wata sanarwa da hukumar ta fitar, ta ce kalubalen tsaro da ake fuskanta a yanzu, ya jefa harkokin yada labarai cikin mawuyacin hali, abun da ke tarnaki ga aikin jarida.

Za a yi amfani da Shirin mai taken 'kafafen watsa labarai da tsaro' ne a lokacin da aka samu barkewar ayyukan ta'addanci a kasar, musammam ma a yankin arewacin kasar dake iyaka da kasashen Mali da Niger.

Cikin 'yan shekarun da suka gabata, kasar Burkina Faso ta yi fama da hare-haren ta'addanci, inda wasu alkaluma a hukumance ke cewa hare-haren sun yi sanadin mutuwar mutane sama da 70 cikin shekarar 2015. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China