in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Batun tsira daga kurkuku ya sake barke a kasar Congo Kinshasa
2017-07-29 13:37:06 cri
An sake samun fursunonin da suka balle daga kurkukun birnin Bukavu na jihar Kivu ta kudu dake gabashin kasar Congo Kinshasa a jiya, al'amarin da ya haddasa mutuwar mutane a kalla 3.

Wani jami'i a birnin ya tabbatar da cewa, a jiya da yamma, fursunonin kurkukun tsakiya na birnin Bukavu, sun tada da bom inda suka yi amfani da shi wajen tserewa daga kurkukun, ya na mai cewa, daga bisani 'yan sanda sun yi kokarin kama su.

Jami'in ya kara da cewa, fursunoni fiye da 20 sun tsere, yayin da wasu 3 suka mutu a lokacin da 'yan sanda ke kokarin kama su, kana wasu sun ji rauni.(Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China