in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
WHO: An shirya don samar da allurar rigakafin Ebola a Congo Kinshasa
2017-05-17 09:44:15 cri
Hukumar Lafiya ta Duniya WHO, ta bayyana a ranar Litinin cewa, yanzu haka ana bincike kan yanayin da ake ciki, game da sake bullar annobar Ebola a kasar Congo Kinshasa, don duba yiwuwar amfani da sabuwar allurar rigakafi wajen tinkarar annobar.

Zuwa yanzu an gano mutane 19 wadanda ake shakkar ko sun kamu da cutar ta Ebola a kasar Congo Kinshasa, cikinsu kuma tuni 3 suka mutu. Ganin haka ya sa kungiyar samar da allurar rigakafin cututtuka ta kasa da kasa, ta tanaji allurar rigakafi guda dubu 300 wadda kamfanin Merck ya samar, sai dai kafin a fara amfani da su, ana bukatar samun izini daga hukumar ta WHO.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China