MSF za ta gudanar da rigakafin cutar zazzabin shawara a Jamhuriyar demokradiyar Congo
Babbar jami'a mai kula da kungiyar agajin likitoci ta Medecin Sans Frontieres MSF, Mrs Axelle Ronsse ta sanar a jiya Laraba cewa, kungiyar agajin ta MSF na kokarin tattara ma'aikata da kuma kayan aiki domin agazawa hukumomin jamhuriyar Congo Kinshasa don yin gangami na masamman na allurar rigakafin cutar zazzabin shawara, inda ake sa ran yi wa sama da mutane miliyan 10 allurar rigakafin cutar cikin kwanaki goma masu zuwa. (Soulayman)
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku