A yau ne aka bude taron dandalin matasan kasashe kungiyar BRICS a nan birnin Beijing, fadar mulkin kasar Sin, inda ake fatan tattauna batun ci gaban matasan kungiyar.
Taken taron na kwanaki uku, shi ne "karfafa hadin gwiwar kungiyar BRICS,da kuma yayata ci gaban matasa." Taron ya kuma hallara wakilan kungiyoyin matasa kimanin hamsin dake aikin gwamnati, da masana, da 'yan kasuwa da masu fasahohi da 'yan jaridu daga kasashen kungiyar ta BRICS. (Ibrahim Yaya)