in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Za a gudanar da taron wakilan kula da harkokin tsaron kasashen BRICS karo na 7 a birnin Beijing
2017-07-24 19:23:28 cri
Za a gudanar da taron wakilan kula da harkokin tsaron kasashen BRICS karo na 7 a birnin Beijing tun daga ranar 27 zuwa 28 ga wannan wata. Wannan taro yana daya daga cikin tarurukan da za a gudanar tun lokacin da kasar Sin ta karbi shugabancin kungiyar BRICS a wannan karo a bana. A kuma saran mamban majalisar gudanarwar kasar Sin Yang Jiechi ne zai shugabanci taron.

Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Lu Kang ya bayyana yayin taron manema labaru da aka gudanar a yau cewa, kasar Sin tana fatan za a kara tabbatar da moriyar juna da sa kaimi ga inganta hadin gwiwa a tsakanin kasashen BRICS a fannin tsaron siyasa, da inganta hadin gwiwarsu ta hanyar gudanar da wannan taro. Daga bisani kuma za a shirya ganawar shugabannin kasashen BRICS da za a gudanar a birnin Xiamen a watan Satumba na bana. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China