in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin na goyon bayan ci gaba da gudanar da yarjejeniyar makamashin nukiliyar Iran
2017-07-22 13:02:10 cri
Shugaban sashen kayyade yawan makamai na ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Wang Yun ya ce, kasar sa za ta ci gaba da goyon bayan kiyaye yarjejeniyar nukiliyar kasar Iran a dukkan fannoni.

Wang Yun ya bayyana haka ne a yayin taro karo na 8, na kwamitin hadin kai game da yarjejeniyar nukiliyar Iran, wanda aka yi jiya Juma'a a birnin Vienna na kasar Austria tsakanin Iran da kasashe 6 da batun nukiliyar ya shafa, da suka hada da Amurka da Burtaniya da Faransa da Rasha da Sin da kuma Jamus.

A cewar Wang Yun, taron ya kasance muhimmin, la'akari da cikar yarjejeniya shekaru 2 da kulluwa.

Ya kuma jaddada cewa, yarjejeniyar na da ma'ana kwarai wajen inganta tsarin hana yaduwar makaman nukiliya, da tabbatar da zaman lafiya da zaman karko a yankin Gabas ta tsakiya, da kuma kiyaye ra'ayin kasancewar bangarori da dama.

Baya ga haka, Wang ya sanar da yadda ake gudanar da ayyukan gyara na'urar sarrafa ruwa mai nauyi ta Arak, yana mai cewa, kasar Sin za ta inganta ayyukan bisa yarjejeniyar da ra'ayin bai daya da bangarori daban daban suka cimma, don kara samun gagarumin ci gaba.

A yayin taron, bangaren Amurka ya bayyana cewa, zai cika alkawarin da ya dauka bisa yarjejeniyar, inda suma sauran bangarori suka jaddada na su goyon baya ga yarjejeniyar. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China