in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin na fatan kasashen duniya za su yi biyayya ga yarjejeniyar nukiliya bayan Amurka ta karawa Iran karin takunkumi
2017-07-19 20:56:17 cri
Kasar Sin ta bukaci daukacin sassa masu ruwa da tsaki, da su maida hankali ga martaba dokokin da suka hana yaduwar makaman nukiliya, ciki hadda martaba yarjejeniyar nukiliyar Iran ta shekarar bara.

Wannan kira dai na zuwa ne, bayan da Amurka ta kakabawa wasu sassa da daidaikun mutane 18 karin takunkumi a ranar Talata. An ce sassan da takunkumin ya shafa dai na da alaka ne da ayyukan kasar da suka shafi sarrafa makamai masu linzami, da wasu makaman wadanda ba na nukiliya ba.

A hannu guda Sin ta bayyana rashin goyon bayan ta, ga duk wasu matakai na yaduwar makaman nukiliya a duniya, ko fakewa da wata dama domin habaka sashen bisa dogaro da dokokin cikin gida.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China