in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilin kasar Sin ya yi kira ga bangarori daban daban da su kiyaye yarjejeniyar Iran
2017-01-19 15:44:43 cri
Mataimakin zaunannen wakilin kasar Sin a MDD, Wu Haitao ya yi kira ga masu ruwa da tsaki a game da batun nukiliyar Iran da su yi kokarin ganin an aiwatar da yarjejeniyar da aka cimma.

Mr Wu wanda ya bayyana hakan a jiya yayin wani taro da kwamitin sulhun MDD ya shirya game da batun nukiliyar Iran, ya bayyana cewa, an aiwatar da yarjejeniyar nukiliyar Iran yadda ya kamata a cikin shekarar da ta gabata, amma duk da haka, akwai matsala da kuma kalubale, wadanda ke bukatar hada kai daga bangarori daban daban.

Wu Haitao ya ce, kullum kasar Sin tana nacewa ga warware batun nukiliyar Iran ta hanyar diplomasiyya da inganta tsarin hana yaduwar makaman nukiliya da kiyaye zaman lafiya a duniya.(Lubabatu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China