A jiya Laraba ne dai aka kaddamar da tagwayen hare-haren ta'addanci a birnin na Tehran. Kana yau Alhamis da maraice, Iran ta sanar da cewa, adadin yawan mutanen da suka rasa rayukansu sakamakon hare-haren ya karu zuwa mutum 17, haka kuma an bayyana takaitaccen tarihin 'yan ta'addan da suka kaddamar da hare haren su biyar. (Murtala Zhang)