in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wang Yi ya yi kira da warware rikicin kasashen yankin Gulf ta hanyar tattaunawa
2017-07-21 09:07:33 cri

Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya yi kira ga daukacin sassa masu ruwa da tsaki da rikicin kasashen yankin Gulf ya shafa da su hanzarta hawa teburin tattaunawa, kana su warware bambance-bambancen dake tsakaninsu karkashin yarjejeniyar hadin gwiwar kasashen yankin (GCC).

Wang ya bayyana hakan ne jiya Alhamis yayin ganawarsa da takwaransa na kasar Qatar Sheikh Mohammed bin Abdulrahman Al Thani wanda ke ziyara a nan birnin Beijing, fadar mulkin kasar Sin.

Ya ce, kasar Sin ta yaba da rawar da kasar Kuwait take takawa na mai shiga na warware wannan takaddama. Ya kuma yi kira ga kasashen duniya, da su taimaka wajen samar da matakan warware wannan matsala a matakin shiyya.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China