in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane 34 sun bace bayan da wani jirgin ruwan soji ya nutse a kasar Kamaru
2017-07-17 20:00:55 cri
Rahotanni daga birnin Yaounde na kasar Kamaru, na cewa a kalla mutane 34 sun bace, bayan da wani jirgin ruwan sojoji ya nutse a yankin tekun Atlantika dake kasar.

Jirgin dai na dauke ne da dakaru 37, ya kuma yi dakon kayan bukatun yau da kullum, da suka hada da abinci, da makamashi, a kan hanyar sa ta zuwa kan iyakar kasar da Nijar.

Da yake tabbatar da hakan a Litinin din nan, ministan tsaron kasar ya ce sojojin da suka bace, na cikin rundunar ko ta kwana ta BIG. A daya hannun kuma, an cimma nasarar ceto wasu sojojin 3 daga tekun na Atlantika bayan da jirgin su ya nutse a ranar Lahadi. (Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China