Rahotanni daga Jamhuriyar Demokuradiyyar Congo(DR Congo) na cewa, a kalla mutane 27 ne suka gamu da ajalinsu kana wasu 54 kuma suka bace, bayan da wani kwale-kwale ya nutse a kogin Kasai ranar Alhamis da dare zuwa wayewar garin Jumma'a .
Kantoman yankin Jacques Mbila ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Xinhua a jiya Lahadi cewa, hadarin ya faru ne sakamakon lodin da ya wuce kima da kuma barasar da matukin ya sha. Ya ce galibin wadanda hadarin ya rutsa da su 'yan makaranta ne dake hutu.(Ibrahim)