in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta bukaci DR Congo ta yi waiwaye kan yarjejeniyar zaman lafiyar kasar
2017-07-12 11:10:53 cri
Wani babban jami'in shirin wanzar da zaman lafiya na MDD ya ce babban abin da zai tabbatar da kawo karshen zaman tankiya game da dambarwar siyasar kasar jamhuriyar demokradiyyar Congo shi ne a sake waiwayar yarjejeniyar da aka cimma tsakanin DRC da abokan hulda na kasa da kasa a ranar 31 ga watan Disambar 2016.

Jean-Pierre Lacroix, mataimakin babban sakataran MDD mai kula da ayyukan wanzar da zaman lafiya shi ne ya bayyana hakan ne a lokacin da yake jawabi ga kwamitin tsaron MDD game da batun na jamhuriyar demokuradiyar Congo.

Game da batun tsaro, jami'in ya ce an samu tabarbarewar al'amurran tsaro ne galibin a yankunan kasar da dama, inda tashin hankali a lardin Kasai ya yi kamari.

Game da matakan da aka dauka a lardin na Kasai, tawagar wanzar da zaman lafiya ta MDD dake kasar Congo (MONUSCO), ta kakkafa kanana da cibiyoyin tafi da gidan ka a yankuna da dama domin tabbatar da tsaron rayukan fararen hula.

Sai dai kuma, duk da irin wadannan yunkuri, ana yawan samun rahotanni na cin zarafin bil adama kuma matsalar na cigaba da ta'azzara a kullum. (Ahmad)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China