in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An fara zaben majalisar dokoki da wasu kananan zabuka a Congo
2017-07-17 09:40:57 cri

Da safiyar ranar Lahadi aka fara kada kuri'u a zaben majalisun dokokin Jamhuriyar Demokradiyyar Congo da wasu kananan zabuka a kasar, sai dai wasu gundumomi 8 na kasar da ake fama da rashin cikakken tsaro wanda mayakan 'yan tawayen ninja suka haddasa, zaben bai gudana ba a wadannan yankuna.

A rumfuna zaben brazzaville, babban birnin kasar, akwai dar dar da ake da shi a sashen arewacin birnin, sai dai an ga cincirundon masu zaben a kudanci inda can ne babbar tungar kungiyoyin 'yan adawar kasar.

Zabukan biyu, ana sa ran mutane sama da miliyan 2 ne za su kada kuri'unsu domin sake zabar mambobin majalisar dokokin kasar su 151, da kuma shugabannin kananan yankunan kasar.

Shugaban tawagar sa ido a zaben daga kungiyar tarayyar Afrika AU, django cissoko, wanda tsohon firaministan kasar Mali ne, ya shedawa kamfanin dillancin labarai na Xinhua cewa, zaben yana gudana, duk da jinkirin fara zaben a kan lokaci da aka samu a wasu wuraren.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China