in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin Libya da MDD ke marawa baya ta kwace iko da filin jirgin Tripoli
2017-06-02 09:43:18 cri
Kwamandan jami'an tsaron fadar shugaban kasar Libya Najmi Nakoo, ya ce iko da filin jirgin saman kasa da kasa na Tripoli ya dawo hannun gwamnatin hadin kan kasar da MDD ke marawa baya.

Yayin wani taron manema labarai a jiya, Najmi Nakoo ya ce hukumomi sun kwace iko da filin jirgin saman kasa da kasa na Tripoli ba tare da sa hannun wata kungiya ba

Kwamandan ya ce dakarun gwamnati sun sake karbe iko da wasu sansanonin soji da wasu wurare dake kudancin Tripoli, wadanda a baya ke hannun kungiyoyin adawa masu dauke da makamai

A ranar 27 ga watan Mayu ne rikici ya barke tsakanin kungiyoyi masu dauke da makamai, inda daya ke mara baya ga gwamnatin hadin kan kasar, yayin da dayar ke goyon bayan hambararriyar gwamnatin Khalifa al-Ghawil, al'amarin da ma'aikatar lafiya ta kasar ta ce yayi sanadin mutuwar sama da mutane 55 tare da jikkata akalla wasu 100.

Tun a shekarar 2011 ne kasar Libya ke fama da rikici tun bayan boren da ya hambarar da tsohon shugaba Muammar Gaddafi.

Kasar dai na kokarin sauya mulki a lokacin da ake tsaka da fuskantar rarrabuwar kawuna tsakanin jam'iyyun siyasa da kuma mamayar kungiyoyi masu dauke da makamai. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China