in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Tashin hankali a Libya ya yi sandin rayuka fiye da 50
2017-05-27 17:40:44 cri
An samu barkewar tashin hankali a jiya Juma'a a Tripoli, hedkwatar kasar Libya, inda bisa kididdigar da hukumar lafiya ta kasar ta yi, lamarin ya yi sanadin rayuka fiye da 50, tare da jikkatar wasu fiye da 100.

An samu tashin hankalin ne tsakanin wata kungiyar masu dauke da makamai, wadda ta kulla kawance da gwamnatin hadakar kasar, da wasu dakaru karkashin kungiyar 'Salvation Government'.

A halin da ake ciki, hukumar lafiya ta kasar ta ce har yanzu tana kokarin tantance hakikanin adadin mutanen da suka mutu ko suka ji rauni.

Bayan barkewar rikicin, gwamnatin hadakar kasar ta yi Allah wadai da dakarun kungiyar 'Salvation Government', wadanda a cewarta suka kaddamar da harin ba tare da la'akari da jama'a ba, har ma aka jefa su cikin wani yanayi mai matukar hadari.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China