in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mataimakin shugaban kasar Sin ya gana da takwaransa na kasar Ghana
2017-06-22 20:48:56 cri
A yau Alhamis, mataimakin shugaban kasar Sin Li Yuanchao, ya yi shawarwari da takwaransa na kasar Ghana Mahamudu Bawumia a nan Beijing fadar mulkin kasar Sin.

Yayin zantawar tasu, Mr. Li Yuanchao ya ce yana fatan bangarorin biyu za su kara amincewa da juna kan harkokin siyasa, da habaka hanyoyin hadin gwiwar moriyar juna a fannonin kudi, da na hada-hadar su, da samar da ababen more rayuwa, da na'urori, da ma'adinai, da makamashi, da kuma aikin gona da na kamun kifi. Kaza lika ya yi fatan za a kara yin musayar al'adu da ta ilmi, domin ciyar da dangantakar sada zumunta dake tsakanin kasashen biyu gaba.

A nasa bangaren, Mr. Bawumia ya bayyana cewa, kasarsa na fatan mayar da martani ga shawarar "ziri daya da hanya daya" karkashin inuwar dandalin hadin gwiwar kasashen Sin da Afirka, domin sada al'ummomin kasashen biyu da tarin alherai. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China