A yau Talata, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Gan Shuang ya shelanta cewa, bisa gayyatar da ministan harkokin wajen kasar Habasha Workineh Gebeyehu da shugaban kwamitin kawancen kasashen Afirka AU Moussa Faki, da ministan harkokin wajen kasar Jordan Aymn Safadi, da ministan harkokin wajen kasar Lebanon Gebran Bassil suka yi masa, ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, zai kai ziyara kasashen Habasha, da hedkwatar AU dake birnin Addis Ababa, da kasar Jordan da kuma Lebanon.
Kaza lika zai halarci taron tattaunawa kan batun rage talauci, da bikin kaddamar da taron dandanlin kwararru da za a yi a Addis Ababa na kasar Habasha. (Sanusi Chen)